Da dumi-dumi - SAUDIYA TA AMINCE DA TASHIN ALHAZAN NAJERIYA DAGA JEDDA

Da dumi-dumi - SAUDIYA TA AMINCE DA TASHIN ALHAZAN NAJERIYA DAGA JEDDA

Labarin dake shigo mana a yanzu nan na cewa hukumar aiyukan Hajj da Umra ta Æ™asar Saudiya ta amince da ci gaba da kwaso mahajjata daga filin jirgi na Abdul Aziz dake Jedda. 
Kamar yadda wani jami'in É—aya daga cikin jiragen da suka yi jigilar mahajjatan wanda kuma jirgin kamfanin na daga cikin jirage 4 da wancan tsari na farko da kasar bayar da aiwatarwa ya shafa, wato, jirgin Max Air, jami'in yace, bayan sun yi taro da hukumar a jiya laraba, a yanzu wannan tsari ya shafi waÉ—anda suka je aikin ne ta jirgin yawo. Masu jirgin yawo ne zasu rika tasowa daga Madina, sauran mshajjata kuwa zasu taso ta inda aka saba, wato, Jedda. 
Indai za'a tuna, farko Æ™asar ta Saudiya ta ce mahajjatan Najeriya da jiragen Aero Air, Air Peace, Max Air da kuma na Azman zasu kwaso mahajjatan ne daga filin jirgin Madina, tsarin da hukumar kula da aiyukan Hajji ta Æ™asa NAHCON ta yi Æ™orafi a kai. 

Post a Comment

Previous Post Next Post