ZA'A YI TARON WAYAT DA KS GA MANOMAN ALKAMA AKWN SANIN DABARUN NOMAN ZAMANI A JAHAR KATSINA

ZA'A YI TARON WAYAR DA KAI GA MANOMAN ALKAMA AKAN SANIN DABARUN NOMAN ZAMANI A JAHAR KATSINA
  
Qungiyar manoman Alkama ta qasa reshen Jahar Katsina ta shirya haÉ—a hannu da wasu hukumonin ayyukan gona  domin bunÆ™asa noman Alkama ka'in da na'in a Jahar a wannan damana. A labarin da muka samu hukumomin da Æ™ungiyar zata yi aikin tare da su sun haÉ—a da Bankin bunÆ™asa Æ™asashen Afirka (African Development Bank) da babban Banking Nigeria CBN da wata Æ™ungiyar larabawa dake Æ™asar Dubai. Shugaban qungiyar noman alkama na jahar Katsina Alhaji Hassan Salihu Æ™wai ne ya bayyana haka a wata hira da aka yi da shi. Alhaji Hassan Salihu Æ™wai ya ce, "maÆ™asudin yin hakan shi ne domin a tallafawa manoman Alkamar na jahar da dabarun noma irin na zamani da bayar da basussuka da nagartattun iri, da samar da taki da sauran tallafi  domin bunÆ™asa noman allkamar.
 Shugaban Æ™ungiyar ya Æ™ara da cewa, tuni Æ™ungiyar ta kammala dukkanin  shirye shiryen da suka dace domin kankamar wannan shirin a jahar ta Katsina. Yace "za a gudanar da wani taron fadakarwa ga  manoman Alkamar a shiyyoyi uku na jahar da suka haÉ—a da Daura da Katsina da kuma shiyyar Funtuwa domin ilmantar da su akan shirin. Alhaji Hassan Salihu ya nuna damuwarsa akan yadda mafiyawan 'yan Æ™ungiyar da suka amfana da bashin Babban bankin Najeriya CBN na "Anchor Borrower" da na "Private Anchor" tun a shekarar 2018 ya zuwa yau basu biya ba". Anan sai yayi kira ga irin waÉ—annan manoman dasu biya waÉ—annan basussuka domin kaucewa É—aukar mataki akan su.
Shugaban kungiyar ya bayyana cewa duk wanda bai biya wannan bashi ba to ba zai amfana da wannan shiri da ake ƙoƙarin gudanarwa domin bunƙasa manoman alkamar ba. Alhaji Hassan yace domin cin nasarar fara gudanar da shirin ƙungiyar ta samar da wasu takardu domin masu bukatar shiga shirin su cika. A ƙarshe Shugaban ƙungiyar ya godewa Babban Bankin Nigeria CBN da Gwamnatin Tarayya da ta jahar katsina akan tallafi da goyon baya da suke baiwa sha'anin noman alkama a jahar katsina.

Post a Comment

Previous Post Next Post